Daga-Abubakar Sale Yakub

Ana sa rai ministocin wajen Turkiyya da na Rasha za su tattauna kan ƙoƙarin kawo ƙarshen yaƙin da ake gwabzawa a Libya, yayin wata ganawa da za su yi ranar Lahadin nan a birnin Istanbul.
Gwamnatin birnin Ankara da takwararta ta Moscow na goyon bayan ɓangarori daban-daban na rikicin, wanda ya yi sanadin raba dubun dabatar mutane daga gidajensu tun daga watan Afrilun bara.
Turkiyya na mara baya wa gwamnati mai sansani a Tripoli, babban birnin ƙasar, yayin da Rasha ke goyon bayan Janar Khalifa Haftar, wanda ya fuskanci ɓacin rana cikin ƴan makwannin nan a hannun dakarun gwamnati.
Duka Turkiyya da Rasha a baya-bayan nan sun ce suna son ɓullo da wnai yanayi na tattaunawa da sasanta tsakani.