Contact Information

114 Lamido Cresent, Giginyu 700213, Kano

We Are Available 24/ 7. Call Now.

An ba da rahoton samun mutane 38 da suka sake  kamuwa da annobar cutar kcoronavirus  a Najeriya, daga cikin sabbin jihohin da cutar ta bulla karon farko akwai Sokoto da Gombe.

Hukumar dakile cutuka masu yaduwa a Najeriya ta ce adadin masu fama da cutar ya zuwa 11:10 na daren Litinin sun kai 665.

Sai dai wani labari mai karfafa gwiwa shi ne a Litinin din nan, an samu mutum 18 rigis da suka warke daga cutar a cewar alkaluman NCDC.

Wannan karo jihar Kano ce ta fi samun yawan mutanen da cutar ta sake kamawa da 23, inda adadin masu annobar a Kano ya kai 59.

Share:

administrator

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *