Contact Information

114 Lamido Cresent, Giginyu 700213, Kano

We Are Available 24/ 7. Call Now.

Gwamnatin Najeriya ta ce ta yi nisa wajen aiwatar da shirinta na tallafa wa kananan masana’antu da masu sana’ar hannu da Naira biliyon saba’in da biyar, kasancewar fiye da mutum 100,000 ne suka ci gajiyar shirin.

Gwamnati na ba da tallafin da nufin rage musu jikkatar da suka yi daga annobar korona.

Gwamnatin Najeriyar ta bayyana cewa a kalla kamfanoni fiye da 25,000 ne suka samu tallafin, wadanda suka hada da kananan masana`antu da makarantun kudi ko masu zaman-kansu, wadanda ke kunshe da ma`ikata fiye da mutum 100,000 da suka fara samun tallafin.

Tallafin, wanda aka kashi gida uku, ma`aikatar da sauran hukumomin da aikin ke wuyansu sun dukufa wajen kaiwa ga kowane rukuni.

Minista a ma`aikatar ciniki da kasuwanci ta kasar, Ambassada Maryam Yalwaji Katagum ta yi wa BBC karin bayani:

“Mun riga mun fara biyan albashi na tallafi na wata uku-uku, an fara biyan watan farko. Kuma mutum ya fi 100,000 wanda aka fara biya.”

Kimanin Naira biliyan 75 gwamnatin Najeriyar ta ware don tallafa wa kananan masana`antu da kuma masu sana`ar hannu.

Gwamnatin na harin tallafa wa masu sana`ar hannu 333,000 ne a kasa baki daya.

Share:

administrator

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *