Contact Information

114 Lamido Cresent, Giginyu 700213, Kano

We Are Available 24/ 7. Call Now.

Daga .Salisu Musa Jegus

Antonio Rudiger ya ce kalaman wariyu sun yi galaba kan karar da ya shigar cewar magoya bayan Tottenham sun ci zarafi ranar 22 ga watan Disamba.
A ranar sai da aka tsayar da wasan da Chelsea ke buga wa da Tottenham, bayan da dan wasan tawagar Jamus ya ce ya ji ana yin kalaman wariya.
Ranar 6 ga watan Janairu, Tottenham ta ce da ita da ‘yan Sanda sun yi dukkan bincike, amma ba su samu gaskiyar zargin da aka yi ba.
Rudiger ya ce ”Ba a hukunta su ba daga karshe, nine da laifi kenan”.
A wani jawabi da Tottenham ta fitar, bayan kalaman Rudiger ta ce ”Ta goyi da bayan matakan da Rudiger ya dauka a halin da ya tsinci kansa kuma suna karfafa gwiwar duk dan wasan da ya ci karo da irin haka nan gaba ya sanar da mahukunta”
Ta kara da cewar ”Komai a fayyace yake kan yadda ta gudanar da bincikin, da zarar ta ci karo da wata shaida ko karin bayani za ta sanar”.

Share:

administrator

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *