Gwamnatin jihar Kano da ke arewacin Najeriya za ta kafa kwalejin horaswa da koyar da dabarun yaki da cin hanci da rashawa karkashin hukumar korafin Jama’a da hana rashawa ta jihar.
Tuni majalisar zartar wa ta Kano ta amince da kafa sabuwar kwalejin koyar da dabarun yaki da rashawar a wani mataki na samar da kwararru kuma managartan Jami’an yaki da rashawa a cewar, Barrister Muhuyi Magaji da ke zaman shugaban hukumar hana ayyukan rashawa ta jihar Kano.
“Yaranmu za su samu horon da ya kamata su samu, sannan su kansu ma’aikata za a horar da su dabarun kaucewa cin hanci da rashawa.” In ji Barrister Magaji.