Contact Information

114 Lamido Cresent, Giginyu 700213, Kano

We Are Available 24/ 7. Call Now.
Ministan Ilimi Adamu Adamu

Ma’aikatar ilimi ta tarayyarNajeriya ta bayar da umarnin rufe duk kan manyan makarantu da Makarantun Sakandire da Primary a wani mataki na kau cewa bazuwar cutar coronavirus.

Wanna na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Ma’aikatar Ilimi na kasa Mista Sonny Echono ya fitar.

A cewar sanarwar da aka fitar a ranar Alhmis , Mista Echono, shine ya bayar da umarnin a madadin Ministan iIimi Malam Adamu Adamu,

Ya kuma sanar da cewa duk kan makarantun Hadaka na tarayya (unity schools ) 104 zasu rufe a yau ko Kafin 26 ga watan Maris 2020, a wani mataki na kaucewa yada cutar covid-19 a Najeriya.

Share:

administrator

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *