Contact Information

114 Lamido Cresent, Giginyu 700213, Kano

We Are Available 24/ 7. Call Now.

Duniya na cikin hadarin fadawa cikin matsanancin farin abinci saboda annobar korona, in ji Majalisar Dinkin Duniya.
Shugaban shirin raba abinci na Hukumar Abinci Ta Duniya David Beasley, ya ce akwai bukatar daukar matakin gaggawa don kaucewa wannan mummunan yanayi.
Wani rahoto da Hukumar ta fitar ya ce, adadin mutanen da ke fama da yunwa a duniya kan iya karuwa daga miliyan 135 zuwa miliyan 250.
Yawancin wadannan mutanen suna rayuwa ne a kasashen 10 da suka fi fama da rikice-rikice da matsalar tattalin arziki da kuma matsalar gurbatar sauyin yanayi.
Wani rahoto da hukumar ta fitar na watanni hudun karshe na bara kan matsalar abinci a duniya ya yi nuni da cewa, kasashen Yemen da Jamhuriyarar Dimokradiyyar Congo da Afghanistan da Venezuela da Ethiopia da Sudan Ta Kudu da Sudan da Syria da Najeriya da kuma Haiti suna cikin barazanar.
A Sudan Ta Kudu, kaso 61 cikin 100 na adadin ‘yan kasar sun yi fama da matsalar abinci a bara, in ji rahoton.

Share:

administrator

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *