Contact Information

114 Lamido Cresent, Giginyu 700213, Kano

We Are Available 24/ 7. Call Now.

Gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ta sanar da ranar kaddamar da ginin layin dogo daga jihar Kano zuwa Maradi a jamhurriyar Nijar, da kuma Kano zuwa Dutse a jihar Jigawa.

A cewar Ministan sufuri, Chibuike Rotimi Amaechi, Buhari da kansa zai kaddamar da fara ginin ranar Talata 9 ga watan Febrairu, 2021.

Amaechi ya sanar da haka a shafinsa na Tuwita.

“Muna farin ciki sanar da kaddamar da ginin layin dogon Kano-Maradi, Kano-Dutse ranar Talata,” yace.

“Shugaban kasanmu, Muhammadu Buhari zai kaddamar. An fara aiki.”

Share:

administrator

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *