An gwada zafin jikin mahajjatan bana sannan aka yi musu gwajin cutar korona a yayin da suka isa birnin Makkah a karshen makon jiya, a cewar kamfanin dillancin labarai na AFP.
Kazalika za a killace mahajjata kafin su soma aikin Hajji sannan a sake yi musu gwaji bayan kammala aikin na Hajji. Haka kuma dole ne mahajjata su sanya takunkumin rufe fuska.
A hirarsa da gidan talbijin na al-Arabiya a farkon mako, Ministan Aikin Hajji Mohammed Saleh Binten ya ce an killace mahajjata a gidajensu kafin a sake killace su na kwana hudu a otal-otal da za su sauka a Makkah.
Saudiyya ta bayar da rahoton mutum 270,000 da suka kamu da cutar korona sannan cutar ta yi ajalin kusan mutum 3,000,inda ta zama daya daga cikin kasashen da suka fi fama da cutar a Gabas Ta Tsakiya.